Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Ƙetare

Mutane 14 sun mutu a Kamaru sakamakon hatsarin mota

Published

on

Akalla mutane 14 ne suka mutu a kasar Kamaru sakamakon wani mummunar hatsarin da wata mota kirar Bus ta yi a yankin arewa maso gabashin kasar.

Wata sanarwa da Ministan sifurin kasar Jean Ernest Massena Ngalle Bibehe ya fitar, ta bayyana cewa hatsarin ya faru ne ranar Talata a kauyen Lom da ke yankin Adamaoua, inda ya ce, wani yaro mai shekara 10 na daga cikin wadanda suka mutu.

Wata majiya a wani asibiti da ke kusa da Garoua-Boulai ta ce, mutane 68 ne suka jikkata a hatsarin.

Tun a baya dai, alkaluman Hukumar lafiya ta Duniya sun nuna cewa kasar Kamaru na daya daga cikin kasashen Afirka da ke kan gaba wajen samun yawaitanrmace-mace a haduran mota.

Ko a shekarar 2018, kasar ta samu mutuwar sama da mutane 7,000 a haduran ababen hawa.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!