Connect with us

Labarai

Fadar Shugaban Kasa ta musanta sauke George Akume daga mukamin Sakataren Gwamnatin Tarayya

Published

on

Fadar Shugaban Kasa ta musanta rahotannin da ke yawo cewa an sauke Sanata George Akume daga mukaminsa na Sakataren Gwamnatin Tarayya (SGF).

A wata sanarwa da mai baiwa shugaban kasa shawara na musamman kan bayanai da dabarun sadarwa, Bayo Onanuga, ya fitar ya bayyana cewa babu wani sabon nadi da shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya yi, yana mai cewa rahotannin da ke yawo kan sauke Akume “labaran karya ne.

Onanuga ya tabbatar da cewa shugaban kasa na ci gaba da kasancewa a kasar Saint Lucia, kuma bai yi wani sauyi ba a cikin mukaman gwamnati.

Fadar shugaban kasa ta bukaci ‘yan Najeriya da su yi watsi da wannan jita-jita da ake yadawa a kafafen sada zumunta

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!