Labarai
Fadar Shugaban Najeriya ta yi kakkausan martani ga Peter Obi

Fadar Shugaban Najeriya ta mayar da martani ga Peter Obi, bayan kalamansa na sukar tafiye-tafiyen Tinubu zuwa ƙasashen waje, tana mai cewa Obi abinda yake faɗa zallar siyasa ne kawai.
Mai taimaka wa shugaba Tinubu kan harkokin sada zumunta, Dada Olusegun, ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Asabar, inda ya kare ziyarar da shugaban ƙasar ya kai taron Africa CEO Forum da aka gudanar a Kigali na ƙasar Rwanda.
Ya ce Tinubu ya jagoranci tawaga ta musamman zuwa Rwanda da ta ƙunshi manyan attajirai da shugabannin masana’antu na kasar nan, ciki har da Aliko Dangote, Abdul Samad Rabiu, Tony Elumelu, Jim Ovia da kuma Wale Tinubu da dai sauran su.
You must be logged in to post a comment Login