Labarai
Hukumar tace finafinai ta Jihar Kano ta dakatar da manyan jaruman Kannywood biyu

Hukumar tace finafinai ta Jihar Kano ta sanar da dakatar da jaruman masana’ntar shirya finafinai ta Kannywood biyu, Adam Garba (Raba-Gardama) da Amina Uba Hassan (wadda tsohuwar matar jarumi Adam A. Zango ce), daga gudanar da harkokin fim a Jihar Kano har tsawon shekara guda.
Sanarwar da hukumar ta fitar ta hannun jami’in hulda da jama’a Abubakar Sani ta ce an ɗauki matakin ne bayan bayyanar jaruman biyu a wani bidiyo da ta bayyana a matsayin wanda ya saɓa da tarbiyya, lamarin da ya jawo ce-ce-ku-ce a tsakanin al’ummar Jihar Kano.
You must be logged in to post a comment Login