Connect with us

Labarai

Sarkin Musulmi a Najeriya ya bukaci a fara duba watan Zulhijja a gobe Lahadi

Published

on

Mai Alfarma sarkin musulmi kuma shugaban majalisar koli ta Harkokin Addinin Musulunci a Najeriya, Muhammad Sa’ad Abubakar na III, ya bukaci al’ummar musulmi a fadin kasar nan da su fara duba jinjirin watan Zulhijja na shekarar 1447 a ranar Lahadi 17 ga Mayun da muke ciki.

Hakan dai na cikin sanarwar da kwamitin harkokin addini na majalisar Masarautar Sokoto ya fitar ta hannun Shugabanta, Farfesa Sambo Wali Junaidu, inda ta ce ranar ta yi daidai da 29 ga watan Zulki’ida na shekarar 1447 bayan hijira.

Sanarwar ta kuma bukaci duk wanda ya ga jinjirin watan da ya sanar da Hakimi ko Dagaci mafi kusa domin isar da bayanin ga Sarkin Musulmi don daukar matakin da ya dace.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!