Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Faransa za ta tallafawa Kano don bunƙasa ilimi

Published

on

Gwamnatin ƙasar Faransa ta yi alƙawarin tallafawa Kano wajen bunƙasa Ilimi.

Jakadan Faransa a Najeriya, Jerome Pasquier ne ya bayyana haka ranar Litinin a Kano, yayin karɓar daliban Kano da suka je ƙaro karatu Faransa.

Jakadan ya ce, shiri ne da Gwamnatin Kano ke yi na ɗaukar nauyin ɗaliban tare da haɗin gwiwar Faransa.

Ya ce, za a faɗaɗa shirin a nan gaba domin manyan makarantun jihar Kano su amfana.

A nata jawabin Kwamishiniyar Ilimi mai zurfi ta jihar Kano, Dakta Mariya Mahmud Bunkure, ta ce, zuwa yanzu haka ɗaliban Kano sama da 60 ne suka ci gajiyar shirin.

Gwamnatocin biyu sun ƙara sabinta yarjejeniyar shirin zuwa shekarar 2024, tare da fatan ɗorewarta a gaba.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!