Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

FIRS ta kara wa’adin biyan haraji ga kamfanonin da ba su biya akan lokaci ba

Published

on

Hukumar tattara kudaden shiga ta kasa FIRS ta kara wa’adin da ta bai wa wadanda suka gaza biyan kudaden haraji na kamfanoni da sauran mutane dai-daiku har zuwa ranar 31 ga watan Agusta mai kamawa.

Shugaban hukumar Muhammad Nami ne ya bayyana hakan ta cikin wata sanarwa da daraktan yada labaran hukumar Abdullahi Ahmad ya fitar ranar Laraba.

Muhammad Nami ya ce wannan wani mataki ne na sauki ga jama’a da hukumar ta bijiro da shi na tallafawa masu biyan haraji, sakamakon illar da annobar cutar corona ta haddasawa al’ummar kasar nan.

To sai dai ya bayyana cewa babu wani shiri na sake tsawaita wa’adin a nan gaba, a don haka duk wanda ake bi bashin ya hanzarta biya don kaucewa fushin hukumar.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!