Connect with us

Labarai

KIRS ta rufe Makarantu da kamfanoni 7 bisa rashin biyan Haraji

Published

on

Gwamnatin jihar Kano ta ce zata dauki  matakin doka wajen rufe duk wani kamfani ko makarata da asibitocin da suka ki biyan haraji. 

Shugaban sashin tabbatar cewa an biya harajin da Gwamnatin Kano ke bin kamfanoni da makarantu da asibitioci har ma da sauran waurare Malam Abbas Saidu, ne ya bayyana hakan bayan da suka rufe wasu kamfanoni da makarantu guda bakwai a Litinin din makon nan.

Abbas Saidu, ya kara da cewa, hukumar ta tattara haraji za ta ci gaba da bibiyar masu wuraren kasuwanci da kamfanoni don tabbatar da cewa suna biyan gwamnatin harajin da ya kamata. 

Haka kuma ya kara da cewa dole ce ta sanya hukumar rufe kamfanonin sakamakon dogon lokacin da suka dauka ba tare da sauke nauyin harajin da ke kansu ba, duk kuwa da damar da hukumar ta basu.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!