Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Gambari ya gana da kwamitin binciken Magu

Published

on

Shugaban ma’aikatan fadar shugaban kasa Farfesa Ibrahim Gambari ya yi wata ganawa ta musamman da ‘yan kwamitin shugaban kasa da ke bincikar zargin dakataccen shugaban hukumar EFCC Ibrahim Magu da aikata almundahana.

Rahotanni sun ce babu karin haske kan batutuwan da suka tattauna, sai dai ana ganin hakan baya rasa nasaba da batun binciken da suke yi kan Ibrahim Magu.

A jiya talata ne dai rahotonni suka bayyana cewa shugaban kasa Muhammadu Buhari ya dakatar da Ibrahim Magu daga mukaminsa na shugabancin hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta EFCC.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!