Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Coronavirus

Da dumi-dumi : Ganduje ya sanya dokar yin kulle a Kano

Published

on

Gwamnan jihar Kano Abdullahi Umar Ganduje ya sanar da rufe jihar na tsahon kwanaki 7 a wani bangare na rage yaduwar Coronavirus a jihar ta Kano.

Bayanin hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da Sakataren yada labaran Gwamnan jihar Kano Malam Abba Anwar ya fitar.

Sanarwar ta kuma ce rufe jihar zai fara aiki ne daga ranar Alhamis 16 ga watan Aprilu zuwa ranar Ashirin da uku ga watan na Afrilu.

Sanarwar ta kara da cewa gwamman na Kano Abdullahi Umar Ganduje ya ce hana shige da ficen zai fara aiki ne daga karfe goma na daren ranar ta Alhamis.

Hakan na zuwa ne dai dai lokacin da aka samu Karin mutum daya dake dauke da cutar inda jumilla suka zama mutane hudu ke dauke da cutar a jihar ta Kano.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!