Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Coronavirus

Da dumi-dumi: Gwamnatin Kano ta tabbatar da karin mutum 5 dake da cutar Corona

Published

on

Ma’aikatar lafiya ta jiha ,ta tabbatar da cewar an kara samun mutum biyar da suka kamu da cutar Corona Virus, a Yanzu haka wanda jimilar ta kawo zuwa yanzu mutum Tara ke dauke da cutar a Kano.

Ma’aikatar ta bayyana haka ne ,a shafin ta na Twitter ,in da ta ce zuwa yanzu haka a yau Laraba an samu karin mutum biyar da aka tabbatar sun kamu da cutar.

Jihar Kano, dai na daya daga cikin jihohin da suke fuskantar barazanar yaduwar cutar ,tun bayan da aka samu mutum daya da ya kamu da ita a farkon makon nan, wanda hakan yasa a jiya Gwamnan jiha Abdullahi Umar Ganduje, ya saka dokar hana zirga -zirga a cikin jihar wacce zata fara aiki a gobe Alhamis da karfe 10 na Daren ranar.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!