Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Manyan Labarai

Ganduje ya sanyawa sabuwar gada sunan Sheik Kariballah

Published

on

Gwamnan jihar Kano Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya sanyawa sabuwar gadar da ake aikin gininta a kan titin kasuwar Rimi sunan shugaban Darikar Kadiriyya na Afrika Sheikh Kariballah Sheikh Nasiru Kabara.

Gwamna Ganduje ya ayyana radin sunan sabuwar gadar ne a yau, a yayin da ya ke jawabi wajen taron Maukibi da mabiya darikar Kadiriyya ke shiryawa a duk shekara.

Gwamna Ganduje ya ce gwamnati ta yi la’akari da irin gudunmawar da Sheikh Kariballah ke bayarwa wajen daukaka addinin musulunci da kuma hadin kan jama’a, shine ma dalilin da ya sanyawa wannan sabuwar gadar sunanasa.

Gwamna Ganduje ya kuma bukaci Sheikh Kariballah da ya ziyarci gurin da ake aikin ginin gadar don ganewa idanun sa yadda aikin yake wakana tare da sanyawa aikin albarka.

Tarihi dai ya nuna cewa wannan shine karo na 69 da mabiya darikar Kadiriyya ke gudanar da wannan taro.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!