Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Kano

An bukaci a daga darajar kwalejin ilimi ta Nasiru Kabara zuwa jami’a

Published

on

Dan majalisar dattijai mai wakiltar yankin Kano ta Kudu Sanata Barau Jibrin ya bukaci shugaban darikar kadiriyya ta Afrika Sheikh Kariballah Sheikh Nasir Kabara da ya daga darajar kwalejin ilimi ta addinin musulunci da ya fara ginawa zuwa jami’a.

Dan majalisa Barau Jibrin ya bayyana hakan ne a wajen bikin Maukibi da mabiya darikar Kadiryya suke gudanarwa duk shekara da aka gudanar a yau.

Sanata Barau Jibrin ya ce abin alfahari ne yadda aka fara samun mutane irin su Sheikh Kariballah da suke da kishin ilimin addinin musulunci suna irin wannan yunkuri na bunkasa addinin musulunci, a don haka ne shima yayi alkawarin rubanya aikin ginin har sau uku matukar aka daga darajar kwalejin zuwa jami’a.

Barau Jibrin ya kuma ce matasa na matukar bukatar irin wadannan jami’o’I na addinin musulunci don kaifafa kwakwalwar su, kan ilimin addinin musulunci da kuma harkokin kimiyya da fasaha

Sanata mai wakiltar kudancin Kano ya kuma nuna takaicin sa kan yadda ake da jami’o’in addinin musulunci biyar kachal a Najeriya a lokaci guda kuma ake da na addinin kirista guda 34, yana mai cewa akwai bukatar al’ummar musulmi su dage wajen gina jami’o’in addinin musulunci.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!