Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Coronavirus

Ganduje ya tabbatar da bullar cutar Corona a Kano

Published

on

Gwamnan Jihar Kano Dakta Abdullahiu Umar Ganduje ya tabbatar da samun bullar cutar Corona a nan Kano.

Abdullahi Umar Ganduje ya bayyana hakan ne lokacin da yake jawabi ga manema labarai dangane da bullar cutar da yammacin yau a nan Kano.

Ya kuma ce wanda ya kamu da cutar tsohon jakadan kasar nan ne a Kasar waje.

Da Dumi-Dumi: An samu bullar Corona Virus a Kano

Ganduje ya kuma sanar da wasu sabbin tsare-tsaren da ya fito da su a nan Kano don ci gaba da yaki da cutar, wadanda suka hadar da hana direbobin adaidaita sahu daukar fasinja sama da daya a cikin baburansu.

Ya kuma ce za’a ci gaba da tattaunawa da malamai da shugabannin kasuwanni da ma sauran masu ruwa da tsaki don ganin an samu nasarar yaki da cutar a nan Kano.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!