Connect with us

Ƙetare

Ghana: Matasa 6 sun rasu 22 sun jikkata a hargitsin da ya faru yayin ɗaukar sabbin sojoji

Published

on

Mutane shida sun mutu yayin da wasu 22 suka samu raunika sakamakon hargitsin da aka samu a wajen ɗaukar aikin soji a Ghana.

Rundunar sojin kasar ta ce, matasa masu neman aikin ne suka ture shingen jami’an tsaro kuma suka yi tururuwa cikin filin wasa na birnin Accra, inda aka samu asarar rayukan.

Rahotonni sun nuna cewa, rashin aikin yi a ƙasar Ghana mai ɗimbin matasa ya kai kashi 32 cikin ɗari, lamarin da janyo cunkoso a cibiyoyin ɗaukar aiki.

Shugaban Ghana, John Mahama, ya ce gwamnatinsa ta ƙudiri aniyar bai wa dukkan matasan ƙasar damar shiga aikin soja.

Hukumomi sun ci gaba da aikin tantance masu neman shiga sojan bayan ƙura ta lafa, inda suka bayar da tabbacin ɗaukar matakan kariya.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!