Connect with us

Labarai

Gobara ta tashi a kusa da ma’aikatar lantarki ta ƙasa a Abuja 

Published

on

Gobara ta tashi a kusa da ma’aikatar lantarki ta ƙasa da ke Maitama a birnin tarayya Abuja.

 

Wannan na cikin sanarwar da Hukumar Agajin Gaggawa ta Najeriya NEMA ta fitar a ranar Talatar makon nan.

Sanarwar ta ce an samu kiran gaggawa da misalin karfe 2 da mintuna 36 na rana, inda NEMA ta hada kai da Hukumar Kashe Gobara ta Tarayya da ta Babban Birnin Abuja tare da tura jami’an ceto zuwa wurin.

 

Masu bayar da agajin sun yi hadin gwiwa wajen taimakawa aikin kashe gobarar da kuma hana yaduwar ta zuwa gine-ginen da ke kusa, lamarin da ya kai ga shawo kan wutar da misalin karfe 5 da mintuna 45 na yamma.

 

Hukumar ta ce an kammala aikin bayan an tabbatar da cewa gobarar ba ta kara yaduwa ba.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!