Connect with us

Labarai

Gwamna Fintiri ya dakatar da Sarki bisa zargin cin Hanci

Published

on

Gwamnan jihar  Adamawa, Ahmadu Fintiri, ya sanar da dakatar da Sarkin Daware, Alhaji Hassan Ja’afaru, ba tare da kayyade lokaci ba bisa zarginsa cin hanci da gazawar shugabanci.

 

Dakatarwar na cikin wasikar da aka sanyawa hannu mai dauke da kwanan watan  ranar 25 ga Afrilu wadda Adama Mamman ta sanya wa hannu tare raba ta ga manema labarai.

 

Ta cikin  wasikar an umarci sarkin da ya mika duk kadarorin gwamnati da ke hannunsa ga sakataren yankin da ya ke jagoranta.

 

An tuhumi  Ja’afaru da laifin kwace gonaki, kin zama cikin masarautar sa da kuma barazana ga zaman lafiya,  da Gwamna  Fintiri ya ce ba za a kyale wani bangare ba wajen yaki da cin hanci da rashawa a fadin jihar Adamawa, koda na gargajiya ne.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!