Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Gwamna Zulum yaƙi amincewa a sanya sunansa a rukunin ɗakunan kwanan ɗalibai

Published

on

Gwamnan jihar Borno Farfesa Babagana Umara Zulum, ya yi watsi da sanya sunansa a wasu rukunin gidajen kwanan ɗalibai guda biyu domin karrama shi.

Rukunin gidajen wanda suke a kwalejin kimiyya da fasaha ta Ramat da ke Maiduguri, mallakin gwamnatin jihar.

Zulum yaƙi amincewar ne a ranar Litinin lokacin bikin ƙaddamar da dakunan kwanan guda 1,500, wanda ma’aikatar ilimi da fasaha da kirkire-kirkire ta jihar ta gyara.

Tunda fari dai an sanya wa tagwayen aikin suna “Injiniya Farfesa Babagana Umara Zulum male students hostel” amma gwamnan ya ƙi amincewa da hakan.

A cewar Zulum “A’a ba zan bari a sanya sunana a duk wani aiki ba da aka gudanar a zamanin da nake kan karagar mulki kamata ya yi a bari sai bayan na bar mulki”.

Gwamna Zulum ya yabawa kwamishinan ilimi mai zurfi a fannin kimiyya, da fasaha da ƙirƙire-ƙirƙire, Injiniya Dr. Babagana Mallambe Mustapha, bisa ga irin rawar da ya taka wajen ciyar da kwalejin gaba.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!