Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Wa zai gaji Ganduje

Published

on

Tun bayan da aka fara kada gangar siyasar tunkarar babban zaben badi a Najeriya, tuni masu neman takara suka fara bayyana aniyar su ta tsayawa takara domin ɗarewa kan kujerar gwamna a Kano.

Wannan dai na nuni da cewa ko wannensu na hanƙoron ganin ya gaji gwamna mai ci a yanzu wato Dakta Abdullahi Umar Ganduje.

Kuma bayyana bukatar ta su ta neman tsayawa takara ta ƙara zaburar da wasu ƴan siyarar wajen ganin sun fito da ta su manufar.

A gefe guda kuma wasu ƴan siyasar na ci gaba kokarin sauya sheƙa daga wadda ta ba su damar ɗare wa kan madafun iko a cikinta zuwa wadda za su sake neman takara a ciki.

Zuwa yanzu dai ba a kai ga kammala sanin adadin masu muradin ɗarewa kan kujerar gwamna a zaɓen 2023 ba.

Sai dai ga wasu daga cikin waɗanda suka bayyana manufarsu kamar haka.

Abdussalam Abdulkarim A.A. Zaura

Alhaji Usman Alhaji

Sanata Barau I. Jibril

Murtala Sule Garo

Kabiru Alhassan Rurum

Alhaji Inuwa Waya

Malam Ibrahim Khalil

Sha’aban Ibrahim Sharaɗa

Muhyi Magaji Rimin Gado

Nasiru Yusuf Gawuna

Abba Kabir Yusuf

Dr Yunusa Adamu Dangwani

Ibrahim Al’ameen Little

Abin jira a gani dai ne shi ne ko wane ne zai samu nasarar ɗarewa kan karagar kujerar gwamnan Kano a 2023.

 

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!