Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

ilimi

Zulum ya dakatar da hukumar gudanarwar kwalejin fasaha ta Ramat

Published

on

Gwamnan jihar Borno Farfesa Babagana Umara Zulum ya dakatar da dukkanin shugabannin hukumar gudanarwar kwalejin kimiyya ta Ramat da ke jihar na tsawon watanni shida.

Gwamnan a wata ziyarar ba-zata da ya kai a ranar Talata ya kadu da ganin yadda dakunan gwaje –gwajen kwalejin suka daina aiki.

Wannan na cikin wata sanarwa da mai taimakawa gwamnan jihar Malam Isa Gusau ya fitar.

A cewar sanarwar, gwamnan ya ziyarci kwalejin kimiyya da misalin karfe 9:00 na safe inda ya ga yawancin dakunan gwaje -gwajen ba sa amfani, inda wasu ke rufe har sun yi yanar gizo -gizo da beraye saboda rashin kulawa.

Idan za a iya tunawa Zulum tshohon dalibin kwalejin kimiyyar ne daga 1986 zuwa 1988 kuma ya taɓa rike mukamin shugaban kwalejin daga 2011 zuwa 2015.

.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!