Labarai
Gwamnan Kano ya yi barazanar tsige jami’an Gwamnati masu saba wa manufofin sa

Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya ce duk wani Kwamishina ko mai ba shi shawara da ya san ba zai iya gudanar da manufofin gwamnatin sa yadda ya kamata ba, ko kuma yana da wata manufa ta daban da za ta kawo tsaiko ga ci gaban gwamnati, to ya gaggauta a jiye muƙaminsa kafin gwamnati ta ɗauki matakin cire shi.
A cewar gwamnan, gwamnatin sa ta zo ne domin samar da ingantaccen shugabanci da kuma kawo sauyi mai amfani ga al’ummar jihar Kano, saboda haka ba za ta bari wasu mutane su yi amfani da muƙamansu wajen kawo ruɗani ko hana aiwatar da manufofin gwamnati ba.
Gwamnan ya kuma gargadi duk wani jami’in gwamnati da ke nuna halin ko-in-kula wajen gudanar da aikinsa da cewa gwamnati za ta ɗauki mataki mai tsauri a kansa, domin al’ummar jihar Kano sun ba su amanar jagoranci ne domin yi musu aiki yadda ya kamata.
You must be logged in to post a comment Login