Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Gwamnan Nasarawa ya kira taron gaggawa kan harin da aka kaiwa mataimakinsa

Published

on

Gwamnan jihar Nasarawa Abdullahi Sule ya kira taron gaggawa kan harin da aka kai wa mataimakin sa Dr, Emmanuel Akabe wanda yayi sanadiyar mutuwar mutane 5.

 

Wannan na kunshe ne cikin sanarwar da sakataren yada labaran sa Yakubu Lamai cewa gwamnan ya kira taron gagawa ne don sake karafafa tsaro a jihar.

 

A yayin taron sa safiyar yau Laraba gwamnan ya baiwa al’ummar jihar tabbacin tsaro da lafiyar ‘yan jihar ta Nasarawa.

 

Rahotanni sun bayyana cewar a dai kwanakin baya ne majalisar dokoki ta jihar ta yi kira ga gwamnan jihar ta sake rubanya kokari kan matsalar tsaro na jihar kasancewar masu satar mutane da yin garkuwa da su, sun yi yawa a jihar ta Nasarawa.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!