Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Kano

Gwamnatin Kano za ta magance fashewar bututun ruwa

Published

on

Gwamnatin jihar Kano ta ce za ta samar da tsaftataccen ruwan sha ga al’ummar jihar na daya daga cikin manyan ayyuka da za ta fi ba da fifiko a shekara mai zuwa.

Kwamishinan albarkatun ruwa na jihar Kano Sadiq Aminu Wali ne ya bayyana haka jim kadan bayan kammala kare kunshin kasafin kudin ma’aikatar gaban kwamitin kula da albarkatun ruwa na majalisar dokokin Kano a jiya litinin.

Ya ce, ma’aikatar za ta zage dantse wajen bullo da shirye-shirye wadanda za su taimaka gaya wajen magance matsalolin da ake fuskanta a bangaren samar da ruwan sha ga al’ummar jihar.

A nasa bangaren shugaban hukumar samar da ruwan sha ta jihar Kano Injinya Garba Ahmed Kofar Wambai, ya yi kira ga al’ummar Kano da su rika sanar da hukumar akan lokaci a duk lokacin da suka samu fashewar bututuwan ruwa a yankunansu.

Wakilin mu na majalisar dokokin Kano Abdullahi Isah ya ruwaito shugaban hukumar WRECA Injinya na cewa hukumar za ta saya sabbin motoci na zamani domin fsukantar kalubalen da ke gabanta.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!