Labarai
Gwamnatin Kano ta fara rangadin kananan Matatun Ruwa domin farfaɗo da su

Gwamnatin Jihar Kano ta fara rangadin duba ƙananan matatun ruwa da ke samar da ruwan sha ga al’ummomin karkara, a wani ɓangare na shirin farfaɗo da cibiyoyin samar da ruwa a faɗin jihar.
Kwamishinan Ma’aikatar Ruwa, Muhalli da Sauyin Yanayi, Dakta Dahir M. Hashim, ya ce an gudanar da rangadin ne tare da Kwamishinan Ma’aikatar Ƙananan Hukumomi da Masarautu, na Ma’aikatar Wuta da Tsaftataccen Makamashi, da kuma na Ma’aikatar Raya Karkara da Ci gaban Al’umma.
A cewarsa, sun ziyarci matatar ruwan Kusalla da ke samar da ruwa ga ƙananan hukumomin Karaye, Kiru da Gwarzo, da matatar ruwan Pada mai samar da ruwa ga Gwarzo, da matatar ruwan Magaga mai samar da ruwa ga Gwarzo da Kabo, sannan da matatar ruwan Guzuguzu mai samar da ruwa ga Kabo da Rimin Gado.
Ya bayyana cewa an tantance matsalolin da kowace matata ke fuskanta tare da tsara hanyoyin gyara da sabunta su, domin gabatar wa Gwamna Abba Kabir Yusuf don amincewa da aiwatar da aikin.
Dakta Dahir Hashim ya tabbatar wa al’ummar jihar, musamman mazauna Karaye, Kiru, Gwarzo, Kabo da Rimin Gado, cewa gwamnatin jihar ta himmatu wajen dawo da cikakken aikin waɗannan matatun ruwa domin samar da wadataccen ruwan sha ga al’ummomin yankunan da abin ya shafa.
You must be logged in to post a comment Login