Connect with us

Labarai

Gwamnatin Adamawa ta sanya dokar hana fita ta sa’o’i 24 a Lamurde

Published

on

Gwamnan Jihar Adamawa, Ahmadu Fintiri, ya sanya dokar hana fita ta awanni 24 a ƙaramar hukumar Lamurde  sakamakon sake barkewar rikicin ƙabilanci a wasu sassan yankin.

 

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Humeashi Wonosikou, ya fitar, gwamnatin jihar ta bayyana rikicin a matsayin abin da ba za a amince da shi ba, tare da umartar jami’an tsaro su tabbatar da bin dokar hana fitan domin dawo da doka da oda.

 

An kuma buƙaci mazauna yankin su bi dokar tare da bai wa jami’an tsaro bayanai da za su taimaka wajen dawo da zaman lafiya, yayin da gwamnan ya jaddada cewa gwamnati za ta ci gaba da kare rayuka da dukiyoyin al’umma.

 

Rikicin dai ya samo asali ne daga arangama tsakanin al’ummomin Chobo community da Bachama community, inda rahotanni suka ce aƙalla mutane biyu sun rasa rayukansu kafin a ayyana dokar hana fitan, yayin da ’yan sanda ke ci gaba da tattara cikakken bayani kan asarar rayuka.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!