Connect with us

Labarai

Gwamnatin Jigawa ta amince da kudirin tilasta yin gwajin ga masu shirin yin Aure

Published

on

Majalisar zartaswar jihar Jigawa, ta amince da kudirin tilasta yin gwajin kwayoyin halitta ga mutanen da ke shirin yin  Aure.

Da ya ke yi wa manema labarai karin haske game da zaman majalisar da ya gudana karkashin jagorancin mataimakin gwamnan jihar ta Jigawa Injiniya Aminu Usman Gumel a gidan gwamnatin jihar da ke Dutse, Sakataren yada labaran gwamnan Malam Hamisu Muhd Gumel, ya ce, an dauki matakin ne domin rage yawan haifar yara masu dauke da cutuka.

Haka kuma, Malam Hamisu Muhd Gumel, ya kara da cewa, majalisar zartaswar ta sake amincewa da bukatar kashe sama da Naira miliyan 300 domn gina wasu cibiyoyin samar da Ruwan sha a sassan jihar.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!