Connect with us

Jigawa

Gwamnatin Jigawa ta ja kunnen Yan Kwangila

Published

on

Ma’aikatar samar da wutar lantaki da makashi ta jihar Jigawa ta ce bazata lamunci yin aiki ba bisa ka’ida ba ga dukkanin dan kwangilar dake aiki a ma’aikatar.

 

Kwamashinan ma’aikatar Injiniya Dakta Surajo A. Musa, wanda ya samu wakilcin daraktan samar da fitulu masu amfani da hasken rana na ma’aikar injiniya Akilu Jafaru Badakaya, ne ya bayyana haka yayin tallata ayyukan kwangila na samar fitulu masu amfani da hasken rana na ayyukan mazabun ‘yan majalisu 30 da ke jihar.

 

Ya ce aikin samar da fitulun zai lakume kudi sama da naira miliyan dubu 887.

 

A nasa jawabin babban daraktan hukumar lura da ingancin ayyuka na jihar Jigawa wanda ya samu wakilcin injiniya Danazumi Musa, yace kamar yanda tsarin hukumar yake zasu cigaba sanya idanu tare da hadin gwiwa da kungiyoyi domin tabbatar da ingancin ayyukan da za’a gudanar.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!