Connect with us

Labarai

Gwamnatin jihar Yobe ta bayar da umarnin rufe duka makarantun sakandiren kwana saboda barazanar tsaro

Published

on

Gwamnatin jihar Yobe ya bayar da umarnin rufe duka makarantun sakandiren kwana da ke faɗin jihar saboda barazanar tsaro.

Cikin wata sanarwa da babban darakta yaɗa labaran gwamnan jihar, Mamman Mohammed ya fitar ya ce gwamnatin ta ɗauki matakin ne domin kare ɗaliban da ke makarantun kwana.

Matakin na zuwa ne bayan da a makon da ya gabata wasu ƴanbindiga suka sace ɗalibai a makarantun kwana jihohohin Naje da Kebbi.

Sanarwar ta ce an ɗauki matakin ne bayan taron ƙoli na tsaron jihar da Gwamnan Mai Mala Buni ya jagoranta, domin nazarin tsaron makarantu a wasu sassan ƙasar.

Sanarwar ta ci gaba da cewa matakin rufe makarantun ya fara aiki ne nan take, har zuwa lokacin da yanayi zai inganta.

Hare-hare kan ɗalibai a makarantu a Najeriya cikin makon da ya gabata, ya haifar da rufe makarantun a wasu jihohin ƙasar da suka haɗa da Neja da Filato da Katsina.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!