Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Tsaro – Gwamnatin jihar Niger ta rufe dukkan makarantun sakandaren Jihar

Published

on

Gwamnatin Jihar Niger ta sanar da rufe makarantun sakandaren Jihar na tsawon makonni biyu, domin baiwa jami’an tsaro damar nazartar halin da ake ciki na kalubalen tsaro, inda aka rinka sace daliban makarantun kwana a wasu Jihohin arewacin Najeriya.

Kwamishiniyar Ilimi ta Jihar Hajiya Hannatu Jibrin Salihu, ta ce za a rufe makarantun daga juma’ar nan 12 ga watan Maris, har zuwa ranar 26 ga Maris din na shekarar 2021.

“Bayan kammala nazartar yanayin tsaron da ake ciki a halin yanzu, za mu samu damar nakaltar hanyoyin domin baiwa al’umma tabbacin tsaron lafiyar ‘ya’yansu, da ta malamai da sauransu” in ji Kwamishiniyar.

“da ma can kuma gwamnan Jihar Abubakar Sani Bello ya ba da umarnin rufe makarantun kwana 11 da na jeka-ka-dawo 11 sakamakon fuskantar klubalen tsaro” a cewar Hannatu Jibrin.

Tun bayan sace daliban makarantar Kagara ne gwamna Bello ya bayar umarnin gaggawa na rufe dukkan makarantun kwana da ke kananan hukumomi hudu na Jihar, da suka hadar da Rafi Munya Mariga da kuma Shiroro.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!