Connect with us

Labarai

Gwamnatin Kaduna ta kwace wasu gidaje da filaye

Published

on

Gwamnan jihar  Kaduna, Sanata Uba Sani, ya bayar da umarnin kwace wasu gidaje da filaye wadanda gwamnatin baya ta raba a cikin harabar makarantu a jihar. 

Bayanin  kwace filayen na kunshe ne ta cikin wata sanarwa da Sakataren gwamnatin jihar, AbdulKadir Muazu Meyere ya fitar. 

Sanar ta ce, matakin kwace filayen ya samu amincewa ne tun a bara, kuma tuni an sanar da wadanda aka sayar wa filayen. 

Sabon matakin ya shafi makarantu irin su Alhuda-Huda College da ke Zariya da kuma Queen Amina College da ke  Kaduna. 

Ita ma makarantar Government Commercial College da ke Zariya na daga cikin wuraren da gwamnatin ta kwace filayen su bayan gwamnatin Nasir El-Rufa’i ta sayar da su a baya.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!