Connect with us

Labarai

Gwamnatin Kano ta ƙaddamar da shirin yaƙi da yin Bahaya barkatai

Published

on

Gwamnatin jihar Kano, ta ƙaddamar da shirin yaƙi da bahaya barkatai a wasu ƙananan hukumomi.

gwamnatin ta bayyana hakan ne ta cikin wata sanarwa da Shugaban Hukumar Samar da Ruwan da Tsaftar Muhalli a yankunan Karkara ta Jihar Kano RUWASSA, Samwilu Abdulkadir Isah, ya fitar.

Ta cikin sanarwar, ya ce, shirin ya shafi ƙananan hukumomin Fagge, Dala, Gwale, Nassarawa, Tarauni, Birni da Kewaye, Garun Malam da Makoda.

Shugaban ya ce, Gwamnan Kano, Engr. Abba Kabir Yusuf, ya amince da shirin, yayin da ma’aikatan RUWASSA za su riƙa zagayawa domin duba wurare da ɗaukar matakan hana bahaya barkatai.

Gwamnatin ta kuma fara shirye-shiryen gina bandakuna a makarantun tsangaya, yayin da RUWASSA za ta duba wuraren da ke fama da gurɓataccen ruwa tare da kai ɗauki da karɓar bayanai daga jama’a.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!