Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Na shirya tsaf domin yakar zazzabin Malaria – Ganduje

Published

on

A baya-bayan nan ne gwamnatin Kano ta sanar da cewa za ta kaddamar da shirin bayar da tallafi ga mata masu juna biyu da kananan yara, yayinda za a yiwa yaran da basu wuce watanni uku zuwa shekarua biyar na haihuwa ba rigakafin zazzabin cizon sauro.

Yayinda kaddamar da shirin raba magunguna rigakafin cutar ta maleriya a jiya Lahadi a garin Bichi, gwamnatin Kano ta ce za ta kashe naira biliyan uku domin shawo kan matsalar zazzabin cizon sauro a fadin jihar.

Gwamnan Kano Dr Abdullahi Umar Ganduje wanda ya bayyana hakan a taron kaddamar shirin, y ace yayinda ake samun yawaitar matsalar zazzabin maleriya, musamman a wannan yanayi na damuna ya sanya gwamnati ta tashi tsaye domin tunkarar matsalar.

Gwamnan ya ce abinda suka fi mayar da hankali a kai shine lafiyar mata masu juna biyu da kananan yara, inda ya ja hankalin iyaye su bawa gwamnati hadin kai.

Shima a nasa jawabin, mai martaba sarkin Bichi Alhaji Nasir Ado Bayero ya yi kira ga mutane, musamman wadanda shirin ya shafa da su rungumi tsarin rigakafin hannu biyu, da kuma bin dokokin yaki da annobar Covid-19 da gwamnatin Kano ta gindaya.

Gwamnatin Kano za a dauki tsawon mako guda ana gudanar da shirin rigakafin zazzabin cizon Sauron a kananan hukumomin Kano guda 44.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!