Labarai
Hukumar Kare Haƙƙin Masu Sayayya ta Jihar Kano ta sauya kalar kayan aikin jami’anta

Hukumar Kare Haƙƙin Masu Sayayya ta Jihar Kano KCPC ta sauya kalar kayan aikin jami’anta daga baƙi zuwa kore.
Hakan na cikin sanarwar da Daraktan Wayar da Kan Jama’a na hukumar, Jamilu Mustapha Yakasai, ya fitar a ranar Alhamis, 30 ga Yuli, 2026.
Shugaban Hukumar, Ibrahim Garba Muhammad, ya bayyana sauyin yayin tattaunawa da manema labarai bayan Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, ya amince da buƙatar hukumar.
Daga yanzu, jami’an KCPC da aka amince su gudanar da aiki za su riƙa sanya koren kayan maimakon baƙaƙen kayan da suke amfani da su a baya.
You must be logged in to post a comment Login