Connect with us

Labarai

Gwamnatin Kano ta aike da sunayen mutum 2 zuwa majalisa domin tantance su a matsayin sabbin kwamishinoni

Published

on

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya tura sunayen Barrister Abdulkarim Kabir Maude, da Dr. Aliyu Isa Aliyu zuwa majalisar dokokin jiha domin tantancewa a matsayin kwamishinoni da kuma mambobin majalisar zartarwa ta jiha.

 

Wannan na kunshe ne cikin sanarwar da mai magana da yawun gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya fitar ranar Asabar.

 

Gwamnan ya jaddada cewa gwamnatinsa na da niyyar ci gaba da zabar matasa masu kwarewa da kishin ci gaban jiha, tare da mayar da hankali kan nagarta, cancanta da gaskiya a shugabanci.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!