Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Kano

Gwamna Abba Kabir ya aika wa majalisa sunayen sabbin Kwamishinoni

Published

on

Gwamnan jihar Kano Engr. Abba Kabir Yusuf, ya aike wa majalisar dokoki sunayen mutane 19 domin tantancewa tare da amincewar naɗa su a matsayin Kwamishinoni.

Gwamnan ya buƙaci tantancewar tasu ne ta cikin wata wasiƙa da ya aike majalisar wadda shugabanta Jibril Isma’il Falgore ya karanta ta a zaman majalisar na yau Talata.

Waɗannan gwamnan ya aika da sunayen nasu sun hada da:

1- Comrade Aminu Abdulsalam
2- Hon. Umar Doguwa
3- Hon. Ali Haruna Makoda
4- Hon. Abubakar Labaran Yusuf
5- Hon. Danjuma Mahmoud
6- Hon. Musa Shanono
7- Hon. Abbas Sani Abbas
8- Haj. Aisha Saji
9- Haj. Ladidi Garko
10- Dr. Marwan Ahmad
11- Engr. Muhd Diggol
12- Hon. Adamu Aliyu Kibiya
13- Dr. Yusuf Kofar Mata
14- Hon. Hamza Safiyanu
15- Hon. Tajo Usman Zaura
16- Sheikh Tijjani Auwal
17- Hon. Nasiru Sule Garo
18- Hon. Haruna Isa Dederi
19- Hon. Baba Halilu Dantiye

Majalisar dokokin, ta sanya gobe Laraba da misalin ƙarfe 10:00 na safe a matsayin lokacin da za ta tantance waɗanda gwamnan ya aike da sunayen nasu.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!