Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

An Tashi Lafiya

Gwamnatin Kano ta ce ana cigaba da samun nasara a ƙoƙarin ta na daƙile cutar Amai da Guda

Published

on

Gwamnatin jihar Kano ta yi ƙarin bayani kan halin da ake ciki game da annobar amai da gudawa, wadda ta ɓullo a wasu yankunan jihar.

A kwanakin baya, aƙalla ƙananan hukumomi 22 ne ke ɗauke da annobar, daga bisani kuma suka koma ƙananan hukumomi 16, sai kuma ƙananan hukumomi 10, sannan a yanzu haka kuma suka koma ƙananan hukumomi 6 kacal ɗauke da annobar.

Kwamishinan lafiya na Jiha Dr Aminu Ibrahin Tsanyawa ne ya bayyanawa Freedom Radio cewa, daga cikin mataken da gwamnati ta ɗauka akwai faɗakarwa akan yadda al’umma za su rinƙa kula da jikin su da kuma abincin su, wanda hakan yasa yayi tasiri matuƙa wajen daƙile cutar.

Kwamishinan ya kuma ƙara da cewa, ba sa karɓar kudi daga wajen masu fama da cutar ta Amai da gudawa, illa ma dai suna basu magunguna kyauta.

 

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!