Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

An fara rigakafin cutar amai da gudawa a Jigawa

Published

on

Gwamnatin jihar Jigawa ta ce ta fara gudanar da aikin rigakafin cutar kwalara a kananan hukumomi uku na jihar.

Babban sakataren hukumar bunkasa kiwon lafiya matakin farko na jihar, Dakta Kabiru Ibrahim ne ya bayyana hakan yayin kaddamar da allurar rigakafin a kauyen Badanda, da ke karamar hukumar Dutse.

Ya ce Gwamnatin Tarayya ta ba da alluran rigakafin kusan miliyan 1 da dubu dari hudu da za a yi wa mutane daga shekara 1 zuwa sama.

Dr Kabiru ya yi bayanin cewa kimanin mutane 720 aka yi niyyar allurar rigakafi ta farko da ta biyu a Birnin Kudu, Dutse da Hadejia.

Ya ce manufar ita ce a takaita barkewar cutar kwalara da ta kashe daruruwan mutane a fadin jihar.

Don haka, ya bukaci mutane da su ba da hadin kai ga kokarin Gwamnati wajen dakile cutar.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!