Connect with us

Kasuwanci

Gwamnatin Kano ta hana yan gwangwan sayo karafa daga jihohin Arewa maso Gabas

Published

on

Gwamnatin jihar kano ta umarci masu gudanar da sana’ar gwangwan a da su dakatar da sayo kayayyakin daga yankin Arewa maso Gabas sakamakon iftila’in da aka samu a kwanan na abubuwan fashewa a cikin kayan gwangwan da suke da alaƙa da yankin.

 

Kwamishinan tsaro na jihar Kano AVM Ibrahim Umaru mai ritaya ne ya bayyana hakan a yau yayin wata ganawa da ƙungiyar masu sana’ar gwangwan reshen Arewa kan irin iftila’in da ya faru a Kano sakamakon kayan gwangwan din.

 

AVM Ibrahim Umaru ya ƙara da cewa an ɗauki wannan mataki ne domin kare rayukan da dukiyoyin al’ummar Kano.

 

Da ya ke jawabi, shugaban ƙungiyar masu sayar da kayan gwangwan na yankin Arewa Alhaji Aminu Hassan ya ce, sun gamsu da umarnin da gwamnatin kano ta bayar na dakatar da shigo da kayan daga yankin Arewa maso Gabas domin kare jihar kano daga barazanar tsaro.

 

Kwamishinan ya kuma gargadi mambobin ƙungiyar da su kasance masu bin umarnin da aka basu domin kare rayuka da dukiyoyin al’umma.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!