Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Gwamnatin Kano ta ja kunnen mutane kan amfani da wuta a lokacin hunturu

Published

on

Gwamnatin jihar Kano ta bukaci jama’ar jihar da su rika kula da yadda su ke mu’amala da wuta a wannan lokaci na hunturu don kaucewa hadarin gobara.

Babban mataimakin na musamman ga gwamnan Kano kan takaita yaduwar masifu Alhaji Idi Bukar ne ya bayyana haka ta cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannunsa.

Sanarwar ta kuma bukaci jama’a da a duk lokacin da aka dauke wutar lantarki su gaggauta kashe na’urorin lantarki da kuma gayyato kwararrun masu gyaran wuta da su rika duba musu ko ya Allah wata matsala ta faru sanadiyar wayar lantarki.

A cewar Idi Bukar ta cikin sanarwar dai, jama’a su daina barin kananan yara na dafa abinci da kuma kashe wuta a duk lokacin da aka gama dafa abinci, yayin da ya kuma ya kuma shawarci shugabannin kasuwanni da su rika kula da tsaron kasuwanninsu cikin dare.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!