Connect with us

Labarai

Gwamnatin Kano ta sha alwashin inganta walwalar daurarru dake gidan gyaran hali

Published

on

Gwamnan Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf ya ce gwamnatinsa za ta duba hanyoyin inganta mutanen da iftila’i rayuwa ya kaisu gidan gyaran hali daban-daban a jihar.

Gwamnan ya bayyana haka ne lokacin da ya ziyarci gidan ajiya da gyaran hali dake janguza a nan Kano da yammacin yau Jumma’a.

Abba Kabir yasha alwashin tabbatar da tsari mai kyau da za’a koyar da matasan sana’oi kafin karewar wa’adinsu a gidan, tare da tabbatar da ingancin abinci, bandakuna da kuma dakunan baccinsu da ilimin harma da Addini.

Ziyarar ta biyo bayan wani rahoto da wata jarida ta wallafa a baya bayan nan, inda aka zargi rashin isasshen abinci da laifukan lalata tsakanin fursunoni a wadannan gidajen gidan gyaran halin.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!