Connect with us

Labarai

Gwamnatin Kano za ta yi taron jin ra’ayin jama’a da masu ruwa da tsaki

Published

on

Gwamnatin jihar Kano za ta yi taron jin ra’ayoyin jama’a da masu ruwa da tsaki kan sauye-sauyen da ake shirin yi a kundin tsarin mulkin ƙasa, domin fitar da matsayar jihar kafin zaman sauraron ra’ayoyi na majalisar dattawa.

 

Babban Daraktan yaɗa labaran Gwamnan Kano Sunusi Bature Dawakin Tofa, ne ya bayyana hakan ta cikin wata  sanarwa da ya fitar.

 

Sanarwar ta ce, an gayyaci wakilan majalisar jiha da ta tarayya da kungiyoyin fararen Hula da kafafen yaɗa labarai da ‘yan kasuwa da shugabannin addini da na gargajiya.

 

Haka kuma, sanarwar ta kara da cewa, an gayyaci ƙungiyoyin kwadago da ƙwararru irinsu Kungiyar Lauyoyi NBA da Kungiyar yan Jarida NUJ da kungiyar Direbobi NURTW da Kungiyar Malamai NUT da Kungiyar Likitoci NMA.

 

Haka kuma sanarwar ta kara da cewa, ana sa ran halartar duk masu riƙe da mukaman siyasa na Kano da tsofaffi.

 

Taron zai gudana a ranar Alhamis 24 ga Yuli ga watan nan da muke ciki da misalin karfe 1:00 na rana a dakin taro na Coronation Hall da ke Fadar Gwamnatin Kano.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!