Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Gwamnatin Katsina zata tura dalibai 40 kasar Masar 

Published

on

Gwamnatin jihar Katsina ta ce ta ware guraben karatu 40 ga ɗalibai ƴan asalin jihar waɗanda za ta tura ƙasar Masar domin karatu a fannin likitanci.

Gwamnatin ta ɗauki matakin ne a lokacin taron majalisar zartarwar jihar wanda gwamna Dikko Umaru Raɗɗa ya jagoranta.

Kwamishinan ilimi mai zurfi na jihar, Farfesa Abdulhamid Ahmed ya ce ‘ƙananan hukumomi 31 za su bayar da sunayen dalibai ɗai-ɗaya, yayin da garuruwan Daura da Funtua za su bayar da sunayen dalibai bibbiyu’.

‘Inda a za’a debi ɗalibai uku cikin ƙwaryar birnin Katsina’.

Sai dai sanarwar tace iya daliban da suka kammala makarantun Gwamnatin ne kadai zasu iya cin gajiyar wannan tsarin tsarin.

 

Rahoton: Yusuf Sulaiman

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!