Connect with us

Labarai

Gwamnatin Najeriya ta jaddada kudirin fitar da mutane miliyan dari a kangin talauci

Published

on

Gwamnatin tarayya ta ce za ta tallafawa kananan hukumomin kasar nan domin ragewa al’umma radadin talaucin da suke fama da shi a yanzu.

Ministan ayyuka na musamman Sanata George Akume ne ya bayyana hakan lokacin da ya karbi bakuncin shugaban hukumar tsara yadda ake kashe kudaden gwamnati Victor Morakwu a ofishinsa a Abuja.

George Akume ya yi kira ga gwamnatocin jihohi da su samar da hanyoyin saukakawa rayuwar al’ummar dake zaune a karkara.

Ministan ya kara da cewa wannan shirin na daya daga cikin alkawuran da shugaba Buhari ya dauka na fitar da mutane miliyan dari daga kangin talauci.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!