Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Gwamnatin Najeriya za ta kara karfafa tsaro a kan iyakokin kasar

Published

on

Gwamnatin tarayya ta ce za ta kara karfafa tsaro a kan iyakokin kasar nan da kasashe 7 na tsandauri da kuma na ruwa domin tabbatar da tsaro da zaman lafiya a Najeriya.

Darakta janar na hukumar kula da iyakoki ta kasa da ke karkashin fadar shugaban kasa Adamu Agaji da takawaransa mai kula da iyakokin ketare Mustapha Ribadu ne suka bayyana hakan a taron bikin ranar iyakoki ta Afirka karo na 11 da aka gudanar a birnin Addis Ababa na kasar Ethiopia.

Sun kara da cewa za su yi aikin ne da hadin gwiwar jami’an tsaro domin samun nasarar kawar da aikata miyagun laifuka a Najeriya.

Matakin na zuwa ne a daidai lokacin da zargi ya yi karfi kan cewa wasu bata-gari daga kasashen ketare na shigowa Najeriya suna aikata ta‘addanci suna kashe mutane da ma sauran laifuffuka.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!