Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Gwamnatin Tarayya ta bude iyakoki 6

Published

on

Hukumar yaki da fasa kwauri ta Nijeriya Kwastam, ta ce gwamnatin tarayya ta sake bude wasu iyakokin kasar nan na tsandauri guda shida ammma bisa tsauraran matakan tsaro.

Mukaddashin shugaban hukumar Wale Adeniyi ne ya bayyana hakan ga manema labaran fadar shugaban kasa, jim kadan bayan kammala ganawa da shugaba Bola Ahmad Tinubu.

Ya kara da cewa iyakokin kan tudu guda shida ne kawo yanzu gwamnati ta ba da umarnin sake budewa, amma za sanya ido sosai wajen hana safarar man fetur zuwa ketare, da ma sauran kayayyakin da aka haramta shigo da su.

Tun a cikin watan Agustan shekarar 2019 ne dai gwamnatin tarayya ta rufe iyakokin kasar nan na kan tudu, da nufin dakile ayyukan fasa kwauri da kuma bunkasa shirin samar da shinkafa ta cikin gida, ko da yake a watan Disambar shekarar 2020 gwamnatin ta sake ba da umarnin bude iyakoki hudu daga cikin su.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!