Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Manyan Labarai

Rahoto: Yawaitar makamai a hannun jama’a na kara janyo tabarbarewar tsaro a Najeriya

Published

on

Yaduwar makamai a hannun mutanen da ba jami’an tsaro ba a Najeriya na ci gaba da karuwa, lamarin ya kara janyo tabarbarewar harkokin tsaro a kasar nan.

Matsalolin sun hadar da satar mutane ana garkuwa da su domin neman kudin fansa, hare-haren ‘yan Boko Haram da ma ‘yan bindiga da kuma makamantansu.

Mallakar bindiga ba tare da izini ba babban laifi ne a Najeriya, wanda yanzu ake ganin yadda bata-gari ke mallakar makaman suna kashe jama’a ba gaira ba dalili.

Wasu lokutan ma da rana tsaka ake ganin ‘yan Boko Haram da ‘yan bndiga da sauran bata-gari suna aikata miyagun laifukan ba tare da wani tsoro ba, inda suke harbe-harbe suna sace mutane suna kuma kona wurare.

Mustapha Isyaku mai fashin baki kan harkokin tsaro, ya ce, rashin cikakken tsaro a kan iyakokin kasar nan na taimakawa wajen safarar makamai.

“Ko a baya-bayan nan rundunar ‘yan sandan Jihar Kano ta kwance wani bam da aka ajiye a wata gona, sannan kuma ta samu nasarar kama wani mutum da ke safarar babura ga ‘yan bindiga a Jihar Zamfara,” a cewar jami’in hulda da jama’a na rundunar DSP Abdullahi Haruna Kiyawa.

Abdullahi Haruna kiyawa ya yi kira ga jama’a da surinka baiwa jami’an tsaro hadin kai ta hanyar bayyana rahoton duk wani abu da ba su amince da shi ba domin gudanar da bincike a kai.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!