Connect with us

Ƙetare

Gwamnatin Saudiyya na shirin fara cin tarar masu aikata rashin ɗa’a

Published

on

Gwamnatin kasar Saudiyya ta sanar da cewa za ta fara kakaba tarar kuɗi kan duk wanda aka samu da aikata ayyukan da suka saba da ɗa’a a cikin al’umma, musamman a lokutan ibada kamar sallah.

 

Hukumomin kasar sun bayyana cewa an ɗauki wannan mataki ne domin kare mutunci da tabbatar da tsaro da kuma samar da zaman lafiya ga jama’a.

 

A cewar sanarwar, duk wanda ya aikata laifin da ya shafi karya dokokin ɗabi’a ko rashin ladabi a wuraren ibada zai fuskanci hukuncin tara, kodayake ba a bayyana takamaiman adadin kuɗin ba.

 

Hukumomin sun kara da cewa matakin ya zama wajibi ne ganin yadda dubban al’umma daga sassa daban-daban na duniya ke taruwa a Saudiyya a lokutan ibada, lamarin da ke bukatar ƙarin tsaurara matakan tsaro da ladabi.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!