Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Coronavirus

Covid-19: Yau za’a bude wuraren ibada a Nijar

Published

on

Gwamnatin jamhuriyyar Nijar ta ce za a bude wuraren ibada daga yau Laraba 13 ga watan Mayu na shekarar 2020, bayan rufesu da akayi na tsawon lokaci domin dakile yaduwar cutar Corona.

Kakakin gwamnatin jamhuriyar Nijar ne ya bayyana cikin wani jawabi da yayi a gidan talabijin na kasar a daren ranar Talata.

Sai dai kakakin gwamnatin ya ce sun umarci dukkan gwamnonin kasar da shuwagabannin kananan hukumomin kan su sanya idanu sau da kafa domin ganin mutane sun yi biyayya ga matakkan da aka zayyana a wuraren ibadar.

Labarai masu alaka:

Covid-19: An sanya ranar komawa makarantu a Nijar

Gwamnan Katsina ya jagoranci tawagar haduwa da takwarorinsu na Kasar Nijar

A wani bangaren kuma gwamnatin ta dauki matakin cire dokar kulle da zaman gida a babban birnin Yamai.

Wakilin Freedom Radio a Nijar Yakuba Umaru Maigizawa ya rawaito cewa gwamnatin kasar ta ce ta dauki wannan mataki ne biyo bayan tattaunawa da shuwagabannin addinai da hukumomin kiwon lafiyar kasar.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!