Labarai
Gwamnatin Tarayya ta ƙara yawan ɗaliban da ake ɗauka a makarantun koyon aikin jinya

Gwamnatin Tarayya ta ƙara yawan ɗaliban da ake ɗauka a makarantun koyon aikin jinya daga dubu Ashirin zuwa Hamsin a duk shekara.
A cewar ta ta yi hakan ne domin magance ƙarancin ma’aikatan lafiya tare da ƙarfafa fannin kiwon lafiya a ƙasar nan.
Ministan Ilimi, Dakta Tunji Alausa, ne ya bayyana hakan yayin wata tattaunawa da manema labarai da ya yi a Abuja.
Ya kuma ce wannan na daga cikin sauye-sauyen da gwamnati ke aiwatarwa domin samar da ƙwararrun ma’aikatan da za su taimaka wajen cimma burin gwamnati.
A cewarsa, gwamnati na ci gaba da zuba jari wajen bunƙasa ilimi da ƙwarewar matasa, musamman a muhimman fannoni da ƙasar nan ke buƙata.
Ya ce baya ga aikin jinya, an kuma ƙara yawan ɗaliban da ake ɗauka a fannonin likitanci, harhaɗa magunguna da likitan haƙora, domin rage ƙarancin ƙwararrun ma’aikatan lafiya a Najeriya.
You must be logged in to post a comment Login