Connect with us

Labarai

Kaduna: Mutane 30 sun rasu sakamakon harin masu dauke da makamai a kauyen Naridon

Published

on

Akalla mutum 30 sun rasa rayukansu a wani hari da wasu dauke da makamai suka kai kauyen Naridon da ke gundumar Kamaru a karamar hukumar Kauru ta jihar Kaduna.

 

Rahotanni sun ce maharan sun kai harin ne da misalin karfe 1:00 na dare, inda suka rika harbin kan main uwa da wabi.

 

Kungiyar Amnesty International ta ce maharan sun bi wasu da suka gudu zuwa cikin daji tare da kashe su, yayin da ake ci gaba da gano karin gawarwaki a gidaje da gonaki.

 

Kungiyar ta zargi gwamnati da gaza kare rayuka tare da bayyana cewa hare-haren makamantan wannan sun sha faruwa a yankin Kudancin Kaduna. Zuwa lokacin wallafa rahoton, rundunar ‘yan sandan jihar Kaduna ba ta fitar da wata sanarwa a hukumance kan harin ba.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!